An umarci mayakan Hamas su sanya damara don ci gaba da yaki

 An gaya wa mayakan Hamas su sanya damara don ci gaba da yaki.



Kasashen duniya na matsa lamba kan Isra'ila da Hamas domin su tsawaita yarjejeniyar tsagaita wuta bayan sun yi musayar karin fursunoni sannan an bar karin kayan agaji sun shiga yankin Gaza da aka mamaye.


Sai dai "Majalisar Yaki" ta Isra'ila ta kammala taronta ba tare da cim ma matsaya kan tsawaita yarjejeniyar ba, kamar yadda TRT World ta fahimta. Wasu kafofin watsa labarai na Isra'ila sun ambato majiyoyi suna cewa "jerin sunayen karin mutanen da Hamas ta nemi a sako bai cka sharudan" Isra'ila ba."

Yarjejeniyar tsagaita wutar za ta daina aiki ne da misalin karfe 7 na safe a agogon Gaza, wato karfe 5 a agogon GMT.

Sashen soji na kungiyar Hamas ya shaida wa mayakansa su daura damarar komawa yaki da Isra'ila idan ba a tsawaita yarjejeniyar ba.


"Al-Qassam Brigades yana umartar dakarunsa su kasance cikin shirin ko-ta-kwana a awannin karshe na karewar yarjejeniyar," in ji sanarwar ya fitar. An bukaci mayaka su shiga cikin "damara har sai an fitar da sanarwa a hukumance game da tsawaita yarjejeniyar tsagaita wutar," kamar yadda sanarwar ta kara da cewa.

Post a Comment

1 Comments