’Ba zan taba yafe wa mazan da suka yi mani ciki ta hanyar fyade ba’ inji gurguwar da wasu maza biyu suka Mata fyade

 ’Ba zan taba yafe wa mazan da suka yi mani ciki ta hanyar fyade ba’ inji gurguwar da wasu maza biyu suka Mata fyade.



Grace (ba ainihin sunanta ba ke nan) na ‘’tsoron maza’’ kuma ta ‘’daina yarda da su’’ bayan da aka yi mata fyade, ta yi ciki sau biyu sannan aka yi watsi da ita.


Grace ta zama gurguwa ce tun tana karama saboda kafarta ta shanye baki daya, sakamakon tangarda da aka samu wajen yi mata allurar rigakafi. Sanadiyar haka, tun shekaru da dama kawo yanzu, mai fama da larurar nakasar tana amfani da keken guragu. Akwai dai mutane kimanin muliyan 30 da ke fama da nakasa a Nijeriya daga cikin al’umar kasar kimanin muliyan 200.


Kamar nakasassu da dama, Grace kan fuskanci kyama da tsangwama da cin zarafi da kuma wariya a cikin al’uma.


To amma wani al’amari da ya matukar girgiza ta shi ne wanda ya faru a wata ranar Lahadi a cikin 2014. Lokacin shekararta 21.


A ranar, ta tafi majami’a kamar yadda ta saba a jihar Bayelsa da ke kudancin Nijeriya, wato inda ta ke zaune. To amma dawowarta gida ke da wuya, ba ta san dawan garin ba, sai wani matashi makwabcinsu ya kira ta zuwa gidansa, wai ta zo ta ‘’taimaka masa da wani abu na gaggawa’’ ba tare da ya fayyace mata takamaimai mene ne ba. Daga nan sai mutumin mai shekaru 30 da ‘yan kai, ya yi mata fyade.


‘’Mun yi ta gwagwagwa da shi, ina kuma yi masa magiya, amma bai saurare ni ba’’ inji Grace. Yayin da ta ke tuna abin takaicin, ta ce ‘’wannan shi ne lokacin da namiji ya taba kwanciya da ni rayuwata kuma na rasa budurcina.’’ Grace ta yi ciki sanadin lamarin na fyade.


Bayan da mai fyaden ‘’ya yi amfani da karfi ya sadu da ni’’ sai ya nemi afuwa yana cewa wai ‘’in yafe masa, aikin shedan ne.’’


Mai larurar ta kara da cewa ‘’na ji tsoron fada wa wani’’ cewa an yi mata fyade saboda fargabar matsalar nuna kyama a cikin al’umma. To amma shiru da Grace ta yi ya zo karshe bayan watanni, lokacin da aka tabbatar tana da ciki a sakamakon gwaji da aka yi bayan da ta yi kukan rashin lafiya. ‘’Ban san ina da ciki ba sai bayan wata shida’’ a cewarta. Daga nan ta ba iyayenta labarin fyaden.


Grace ta ce mutumin da ya yi mata fyaden bai musanta ba lokacin da ta shaida masa cewa ta yi ciki, to amma sai ‘’ya yi batan dabo’’ daga unguwar.


Bayan shekara bakwai, a 2021, Grace ta sake fuskantar makamancin wannan yanayi na fyade lokacin da wani makwabcinsu na daban, shi ma ya yaudare ta zuwa gidansa a kekenta na guragu.


Ta haifi gawawwaki ne a duka cikin guda biyu da ta samu sanadin ayyukan fyaden bayan tangardar nakuda a asibiti. Grace ta ce ‘’ni kaina na kusa mutuwa’’ a lokacin nakuda. A ciki na farko, likitoci sun ce ‘’jaririn ya dade ma da mutuwa a cikina.’’


’Ba zan taba yafe wa mazan da suka yi mani ciki ta hanyar fyade ba’


Matar mai nakasa ta ce ta yi tunanin kai wa ‘yan sanda rahoton fyaden da aka yi mata amma sai iyayenta suka ce kar ta yi haka domin ‘’bai wajaba ba’’ kuma ba su da kwarin gwiwar cewa za a yi adalci. A maimakon haka sai suka mayar da hankali wajen kula da cikin da kuma lafiyarta.


Wadda aka yi wa fyaden ta yi watsi da bukatar afuwa daga mazan da suka yi mata fyaden domin a cewarta neman afuwar abu ne da ba za ta iya fahimta ba. Ta yi imanin da gangan suka aikata, don haka ta ce ‘’ba zan taba yafe masu ba.’’


Grace dai daya ce tak cikin dimbin mata da ‘yan mata masu larurar nakasa da ke fama da matsalar fyade da cin zarafi a Nijeriya - lamarin da ke haifar masu da munanan illoli.


A cewar Majalisar Dinkin Duniya hadarin fyade da mata da yara mata masu larurar nakasa ke fuskanta ‘’ya kai ninki uku’’ na wadanda ba su da nakasa ke fuskanta, kuma ‘’sun fi yiwuwar fuskantar cin zarafi na tsawon lokaci da kuma raunuka masu tsanani.’’

Post a Comment

0 Comments