Dakarun Isra'ila sun kutsa kudancin Gaza, kungiyoyin ba da agaji sun yi 'gargadi'


 Dakarun Isra'ila sun kutsa kudancin Gaza, inda dubban fararen-hula suka tsere domin neman mafaka daga luguden wutar Isra'ila da kuma gumurzu tsakanin Isra'ila da kungiyar Hamas mai fafatukar kare hakkin Falasdinawa.



Kungiyoyin bayar da agaji sun yi kakkausan gargadi game da "matsalar rashin jinkai" da ake fama da ita a Falasdinu, suna masu cewa yankin yana dab da fadawa cikin yunwa da cututtuka.


Hamas ta ce Isra'ila ta kaddamar da jerin "manyan hare-hare" a Khan Younis da kuma hanyar da ta hada birnin da Mashigar Rafah, a kusa da kan iyaka da Masar.


Wani wakilin AFP ya bayar da labari kan luguden wutar ya mamaye kudancin Gaza da sanyin safiyar Lahadi.

Post a Comment

0 Comments