Hamas ta yi maraba da matakin Houthi na hana jiragen ruwan Isra'ila wucewa ta Bahar Maliya

 Hamas ta yi maraba da matakin Houthi na hana jiragen ruwan Isra'ila wucewa ta Bahar Maliya



Kungiyar Hamas da ke fafutukar kare hakkin Falasdinawa ta yi maraba da sanarwar da kungiyar Houthi ta kasar Yemen wadda Iran ke marawa baya ta fitar ranar Lahadi da ke cewa za ta hana hana jiragen ruwan Isra'ila wucewa ta Bahar Maliya.


Wata sanarwa da Hamas ta fitar ta jawo hankali game da sanarwar ta Houthi wadda ke cewa: "Idan ba a bari an shigar da kayan bukatu, ciki har da abinci da magunguna, zuwa Gaza ba, za a hana jiragen Isra'ika wucewa ta Bahar Maliya ko da kuwa na kowacce kasa ne."


Kungiyar ta yi jinjina game da wannan "mataki na rashin tsoro" da aka dauka kan hare-haren da aka kwashe fiye da wata biyu ana kaiwa Gaza sannan ta yi kira ga kasashen Larabawa da na Musulmai su cika alkawuran da ke rataye a wuyansu na tarihi don kawo karshen kawanyar da aka yi wa Gaza.


Kakakin kungiyar Houthi, Yahya Saree, a baya ya wallafa sako a shafinsa na soshiyal midiya da ke cewa za su hana jirage bi ta Bahar Maliya domin zuwa Isra'ila idan ba a bari an shigar da kaya irin su abinci da magunguna cikin Gaza ba.


Shugaban Houthi Abdulmalik al Houthi ya yi barazanar kai hari kan jiragen ruwan Isra'ila da ke Bahar Maliya a wani jawabi da ya gabatar ta gidan talbijin ranar 14 ga watan Nuwamba.

Post a Comment

0 Comments