Jajircewar Falasɗinawa ta sa Biden ya gane yaƙin da Isra'ila ke yi a Gaza "hauka ne" : Hamas

 Jajircewar Falasɗinawa ta sa Biden ya gane yaƙin da Isra'ila ke yi a Gaza "hauka ne" : Hamas



Juriya da tsayin daka na al'ummar Falasdinu ya sa shugaban Amurka Joe Biden ya fahimci "haukar" sojojin Isra'ila a mamayar da suke yi a Gaza, in ji wani babban shugaba a Hamas.


Osama Hamdan ya bayyana hakan ne a wani taron manema labarai a birnin Beirut a lokacin da aka tambaye shi game da wani sharhi da kamfanin Biden ya yi a safiyar ranar cewa Isra'ila na rasa goyon bayanta a duniya.


Harin na Isra'ila "zai haifar da mummunan sakamako" kan Isra'ila da kuma yiwuwar sake zaben Biden, in ji shi.


Ya yi nuni da cewa akwai saɓani ƙarara a cikin kalaman na Biden, yana mai cewa a jiya ya tabbatar da cikakken goyon bayansa ga Isra'ila kuma a yau ya bayyana cewa Isra'ila ta fara rasa goyon bayan kasashen duniya.


Biden ya ce gwamnatin Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu na rasa goyon bayanta a duniya kuma "dole ne Netanyahu ya ƙarfafa tare da sauya" gwamnati don "nemo mafita ta dogon lokaci kan rikicin Isra'ila da Falasdinu."

Post a Comment

0 Comments