Sojojin Isra'ila sun 'sace jarirai Falasdinawa, sun fitar da su daga Gaza'

 Sojojin Isra'ila sun 'sace jarirai Falasdinawa, sun fitar da su daga Gaza'



Sojoji Isra'ila sun sace wasu jarirai Falasdinawa sannan suka fitar da su daga Gaza, a cewar wata kungiyar da ke kare hakkin dan'adam, inda ta yi kira ga Isra'ila ta mayar da yaran wurin iyayensu.


Kungiyar Euro-Med Human Rights Monitor mai hedkwata a Geneva a wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na intanet ta ce ta "dauki bayanin da aka watsa a Gidan Rediyon Sojojin Isra'ila ranar 1 ga watan Janairu na 2024 game da sace wata jaririya Falasdinawa daga gidansu a Gaza da wani sojan Isra'ila mai suna Harel Itach, da ke rundunar Givati tare da kashe iyayenta da matukar muhimmanci."


"Bayan samun labarin mutuwar wani sojan Isra'ila ranar 22 ga watan Disamba na 2023 sakamakon raunukan da ya samu a yakin Gaza, abokin Itach ya bayyana batun satar jaririyar inda ya ce ba a san inda take ba," in ji sanarwar.


Kungiyar ta nuna "matukar damuwa" game da hakan, tana mai cewa jaririyar ba ita kadai sojojin Isra'ila suka sace ba.


"Shaidu da dama da mutane suka nuna wa kungiyar kare hakkin dan'adam sun bayyana yadda sojojin Isra'la suke kama kananan yara Falasdinawa su tsare su, sannan su fitar da su daga yankinsu zuwa wani wuri da ba a sai ba," in ji kungiyar.

Post a Comment

0 Comments