Tinubu na fuskantar matsin lamba don dakatar da Betta Edu.

 Tinubu na fuskantar matsin lamba don dakatar da Betta Edu.



Kwanaki ƙalilan bayan hukumar EFCC ta gayyaci tsohuwar ministar jin-ƙai ta Najeriya Sadiya Umar Farouk kan zargin ɓarnatar da wasu kuɗaɗe, sai ga shi sabuwar ministan jin-ƙan, Betta Edu na ƙoƙarin wanke kanta daga zargin sabuwar badaƙala a ma'aikatar.


Hakan na zuwa ne bayan fitar wata takardar biyan kuɗi da ministar ta aike wa ofishin babbar akanta janar da ƙasar, inda a ciki take buƙatar a tura zunzurutun kuɗi har naira miliyan 585, 189,500, don biyan tallafi, a wani ɓangare na tallafa wa masu tsananin buƙatar tallafi a wasu jihohin kasar huɗ.


To sai dai wani abu da ya ja hankali game da biyan kuɗaden shi ne sunan asusun bankin da aka biya kuɗin na wata mata ce mai suna Onlyelu Bridget Mojso.


Tuni dai ofishin babar akanta janar ta ƙasar ya ce ba ya biyan kuɗin gudanar da wani aiki na gwamnati a asusun wani mutum.


Wannan batu dai ya janyo ce-ce-ku-ce a ƙasar musamman a shafukan sada zumunta inda mutane da dama ke kiran shugaban kasar Bola Tinubu ya sauke ministar daga mukaminta

Post a Comment

0 Comments