Asibitin Nasser na Gaza ya zamo dandalin mutuwa — MDD

 Asibitin Nasser na Gaza ya zamo dandalin mutuwa — MDD



Wani jami'in ofishin kula da ayyukan jinƙai na Majalisar Ɗinkin Duniya, OCHA ya bayyana damuwarsa kan halin da Asibitin Nasser ke ciki a birnin Khan Younis a kudancin Gaza da aka yi wa ƙawanya.

"Yanayin da ake ciki yana da ban tsoro. Akwai gawawwaki a barbaje a kan hanyoyi. Marasa lafiya na cikin mawuyacin hali," in ji Jonathan Whittall, babban jami'in kula da ayyukan jinƙai na OCHA a yankin Falasɗinawa da aka mamaye.

Ya ƙara da cewa "Wannan waje ya zamo dandalin mutuwa, ba wajen warkar da marasa lafiya ba."


Isra'ila ta kai hari matsugunin ƙungiyar likitocin MSF a Gaza

Isra'ila ta kai hari a wani matsugunin ƙungiyar agaji ta Doctors Without Borders (MSF) a Gaza da aka yi wa ƙawanya, inda ta kashe aƙalla mutane biyu.

"A daren yau, sojojin Isra'ila sun kai wani samame a Al Mawasi, Khan Younis a Gaza, inda aka harba makamai wani matsuguni da ke karɓar baƙuncin ma'aikatan MSF da iyalansu," in ji MSF a shafin X.

“Yayin da ake ci gaba da samun cikakken bayani, yanzu haka ma’aikatan motar daukar marasa lafiya sun isa wurin, inda aka kashe akalla ‘yan'uwan abokan aikinmu biyu tare da mutane shida da suka ji rauni. Mun firgita da abin da ya faru,” in ji sanarwar.


Post a Comment

0 Comments