Isra'ila ta ji wa wakilan Al Jazeera biyu 'mummunan rauni'

 Isra'ila ta ji wa wakilan Al Jazeera biyu 'mummunan rauni'



Kafar watsa labarai ta Al Jazeera a ranar Talata ta ce an raunata ƴan jaridarta biyu a wani hari da Isra’ila ta kai a birnin Rafah da ke kudancin Gaza.

Kafar watsa labaran ta ƙasar Qatar ta ce rayuwar wakilinta Abu Omar na cikin hatsari sakamakon an yanke ƙafarsa ta dama.

Haka kuma akwai wani wakilinta mai ɗaukar hoto Ahmad Matar wanda ya samu rauni mai yawa tare da zubar da jini. A ƴan kwanakin nan Isra’ila na zafafa hare-hare a birnin Rafah wadda ke kan iyaka da ƙasar Masar.

Post a Comment

0 Comments