Isra'ila ta kashe sama da Falasɗinawa 100 a Rafah

 Isra'ila ta kashe sama da Falasɗinawa 100 a Rafah



Sama da mutum 100 Isra'ila ta kashe a hare-haren da ta kai a birnin Rafah da ke kudancin Gaza, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na WAFA ya ruwaito.

Birnin na Rafah na daidai iyakar ta Gaza da Masar, wanda wuri ne wanda sojojin Isra'ila suka tilasta wa farar hula gudun hijira inda suke inda suka yi iƙirarin cewa wuri ne mai aminci.

Sojojin Isra'ila a ranar Lahadi sun amince da a kai hari ta ƙasa a Rafah.

Falasdinawa sun nemi mafaka a Rafah a daidai lokacin da Isra'ila ke ci gaba da luguden wuta a sassan Gaza tun daga ranar 7 ga watan Oktoba.

Post a Comment

0 Comments