Shekaru uku da rasuwar Farfesa Dahiru Yahaya

 Shekaru uku da rasuwar Farfesa Dahiru Yahaya



Muna addu'ar Allah ya jikansa da Rahama. 


Fafesa Dahiru Yahaya Malamin Jami'a ne kuma masanin tarihi. Kuma Malamin Malamai ne da ya kware a fanninsa. Kafin rasuwarsa ya kasance Fafesa ne a sashen nazarin tarihi a jami'oin Bayero dake Kano da Ahmadu Bello dake Zariya. 


Bayanai sun nuna cewa an haife shi ne a garin Kano a ranar 30 ga wata Yunin 1947. Ya yi karatun digirinsa na farko a bangaren nazarin tarihi a Kwalejin Bayero (Jami'ar Ahmadu Bello a yau) a shekarar 1970. Ya kammala digirin digirgir dinsa ne a bangaren diflomasiyyar tarihi a Jami'ar Birmingham dake Birtaniya a 1975. 


Ya yi aiki a matsayin mataimaki na jin dadi da walwalar jama’a a karkashin gwamnatin yankin Arewa da ke Kaduna. Sannan ya yi aiki a matsayin jami’in gudanarwa a karkashin gwamnatin jihar Kano. 


Dahiru Yahaya ya soma karantawa ne a sashen nazarin tarihi dake Tsangyar Fasaha da nazarin addinin Musulunci na Jami’ar Bayero ta Kano a shekarar 1970 inda ya yi aiki na tsawon rayuwarsa.


Ya rasu ne a ranar Laraba 3 ga watan Fabarairun 2021 bayan ya yi fama da gajeruwar rashin lafiya a jihar Kanon Nijeriya. 


Ya rasu yana da mata 3 da 'ya'ya 24.

Post a Comment

0 Comments