Tankokin yaƙin Isra'ila sun yi wa asibitin Nasser da ke Gaza ƙawanya

 Tankokin yaƙin Isra'ila sun yi wa asibitin Nasser da ke Gaza ƙawanya


Gomman tankokin yaƙin Isra’ila da motoci masu sulke sun yi wa asibitin Nasser da ke Gaza ƙawanya, wanda wuri ne da dubban Falasɗinawa ke neman mafaka, kamar yadda shaidu suka tabbatar.

Waɗanda suka shaida lamarin sun bayyana wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa an buɗe wuta kan ginin asibitin da ke kudancin Khan Younis, amma sojojin ba su kutsa ciki ba.

Ma’aikatar Lafiya ta Gaza ta bayyana cewa sojojin Isra’ila sun ta harbi tare da kai samame a kewayen asibitin domin shirya kutsawa cikin asibitin.

Ma’aikatar ta kuma tabbatar da cewa akwai dubban mutanen da suka rasa muhallansu waɗanda suka samu mafaka a asibitin kuma suna fama da ƙarancin ruwa da abinci.

Post a Comment

0 Comments