Isra'ila ta kashe ƙarin ƴan jarida biyu a Gaza

 Isra'ila ta kashe ƙarin ƴan jarida biyu a Gaza


Isra’ila ta kashe ƴan jarida biyu a Zirin Gaza, wanda hakan ya kawo jumullar adadin ƴan jaridar da ƙasar ta kashe tun daga 7 ga watan Oktoba zuwa 140, kamar yadda Ma’aikatar Watsa Labarai ta Gaza ta tabbatar a ranar Laraba.

Mohammad Al-Sayyed Abu Skheil da Tareq Abu Skheil, waɗanda masu ɗaukar rahoto ne na gidan rediyon Al-Quds Voice Radio, sun rasu ne a lokacin da Isra’ila ta kai hari a asibitin Al-Shifa da ke Gaza, kamar yadda ofishin watsa labaran ya tabbatar a wata sanarwa a ranar Laraba.

Sojojin na Isra’ila sun janye daga asibitin a ranar Litinin da safe bayan sun shafe mako biyu a wurin. Sojojin sun kashe gomman mutane a asibitin baya ga lalata wurare a cikin asibitin.

Post a Comment

0 Comments