Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Abuja ta umarci cafke tsohon hafsan sojojin ruwa a Najeriya.

 Babbar Kotun Tarayya da ke zamanta a Abuja ta umarci cafke tsohon hafsan sojojin ruwa a Najeriya. 

Jaridar Leadership ta ce kotun ta bukaci a kama Vice Admiral Usman Jibrin da wasu mutane biyu kan badakalar makudan kudi har N1.5bn.

Mai Shari'a, Inyang Ekwo shi ya ba da wannan umarni a yau Juma'a 3 ga watan Mayu a Abuja.

Hukumar yaki da cin hanci ta ICPC ita ta gurfanar da mutanen uku a gaban kotu kan almundahana da makudan kudi.

Kotun ta ba da umarnin cafke mutanen bayan karbar korafi mai lamba FHC/ABJ/CR/158/2023 daga lauyan hukumar mai suna Osuobeni Ekoi Akponimisingha.

Lauyan ya gurfanar da Usman Jibrin Oyibe da Adam Imam Yusuf da Burgediya-janar Ishaya Gangum Bauka. Ana zargin mutanen da ba da bayanan karya ga kamfanoni da suke da hannun jari a ciki. 

Kamfanonin sun hada da Lahab integrated da Multi Services Limited da Gate Coast Properties International Limited da Ummays Hummayd Energy Ltd.

Post a Comment

0 Comments